5 Yuni 2017 - 12:54
Nigeria Ba Ta Halarci Taron ECOWAS A Liberia Wanda Natanyahu Ya Halarta Ba

Babu wani jami'an gwamnatin Nigeria da ya halarci taron shuwagabannin kungiyar ECOWAS na kwanaki biyu a birnin Monrovia babban birnin kasar Liberia na kwanaki biyu.

Jaridar Daily Trust ta Nigeria ta bayyana cewa tsohon shugaban kasar Olushegun Obasanjo ya halarci taron na ranakun asabar da lahadi, amma babu wani wakilin gwamnatin Nigeria a taron, wanda a karon farko ya sami halattar Priministan HKI Benyamin Natanyahu.

Majiyar ta bayyana cewa rashin halattar wani jami'in gwamnatin Nigeria a wannan taron ba zai rasa nasaba da halartan Priminisyan yahudawan ba. Duk da cewa duk kokarin da jaridar tayi don samun dalilan hakan bai cimma nasara.288